DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dikko Radda ya nada sakataren gwamnatin Katsina da wasu mukamai 10

-

Google search engine

Sabon Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya amince da nadin Arch Ahmad Musa Dangiwa a matsayin sakataren gwamnatin jihar.

A cikin wata sanarwa da Dikko Radda ya sanya wa hannu, ta ce Gwamnan ya kuma nada Jabiru Tsauri a matsayin shugaban ma’aikatan gidan gwamnati. Kazalika, sanarwar ta ce, Gwamnan ya nada Barr Mukhtar Aliyu a matsayin mataimakin shugaban ma’aikatan gidan gwamnati, sai Abdullahi Aliyu Turaji a matsayin PPS.

Sauran nade-naden su ne na Malam Maiwada Danmalam a matsayin Darakta Janar mai kula da kafafen yada labarai, Sai Ibrahim Kaula Mohammed a matsayin mai magana da yawun Gwamna da Abubakar Badaru Jikamshi a matsayin mataimaki na musamman ga Gwamna kan kafafen yada labarai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara