DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An samu karin jam’iyyar siyasa a Nijeriya

-

Hukumar zaben Nijeriya INEC ta sanar da rajistar sabuwar jam’iyyar siyasa mai suna  wato Youth Party (YP).
A cikin sanarwar da kwamishinan hukumar Festus Okoye ya fitar a Abuja, ta ce hukumar ta yi hakan ne karkashin sashen doka na 225 (a) na kundin tsarin mulkin 1999 da aka yi wa kwaskwarima.
Ya zuwa yanzu dai, akwai jam’iyyun siyasa 19 a Nijeriya  bayan soke rajistar jam’iyyu 74 da hukumar ta yi a shekarar 2020 da aka samu da gaza wani katabus a zaben 2019.
A zaben 2019 dai, jam’iyyu 91 ne suka shiga aka dama da su a zaben.
Festus Okoye ya tunaso cewa a watan Agustan 2018 aka yi wa YP rajista domin bin umurnin kotu da ta yi hukunci a 2017.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara