DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya ta ji kunya a idon duniya – Obasanjo

-

Tsohon shugaban kasar Nijeriya Olusegun Obasanjo ya ce shekaru 63 da samun ‘yancin kan kasar, har yanzu ba ta yi wani abin a zo a gani ba.
Obasanjo na magana ne a Abuja wajen kaddamar da littafin da tsohon ministan ciniki da masana’antu Olusegun Aganga ya rubuta.
Ya ce a lokacin da kasar ta samu ‘yancin kai, ta zamo wata tauraruwa mai haske. Ya ce idan ana son gyara kasar, dole ne sai shugabanni sun amsa laifin cewa akwai matsala.
“Mun ji kunya, mun sa nahiyar Afrika ta ji kunya, mun sa bakaken fata sun ji kunya sannan mun ji kunya a idon duniya”. In ji Obasanjo.
Tsohon shugaban kasar ya ce kasar ba ta ajiye kowace kwarya a gurbinta. Ya ce son zuciya ya dabaibaye kowa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara