DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Katsina ya umarci a fitar da hatsi buhu dubu 36 domin raba wa al’ummar jihar kyauta

-

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD ya umurci da a fitar buhunan hatsi 36,100 domin raba wa masu karamin karfi su samu saukin rayuwa.
Malam Dikko Umaru Radda ya ce ya umurci kananan hukumomi 34 na jihar da su je su sayi masara domin raba wa mabukata su samu sa’ida a rayuwar yau da kullum.
Ya ce an yanke shawarar yin hakan ne domin mutane su samu saukin rayuwa da cire tallafin man fetur ya jawo musu. Ya ma kara da cewa kowa shaida ne ana cikin mawuyacin hali.
Malam Dikko Umaru Radda ya ce gwamnatin tarayya za ta sayar wa gwamnatoci n jihohi da masara, shinkafa da taki, amma a jihar Katsina, za a raba wa talakawa kyauta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara