DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kama mutanen da suka yi wa Sarkin Kano rashin kunya

-

https://drive.google.com/uc?export=view&id=1odnVNqLO5O-OkoSmTf6StxjAPN2U1IY3
Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta ce ta yi nasarar kama karin wasu mutane uku da ake zargi da kalaman batanci ga Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Bayero.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Usaini Gumel, ne ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Kano.
Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa tun farko rundunar ta kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a lamarin.
Gumel ya bayyana sunayen wadanda ake zargin kamar haka; Abdulrazak Usman Sarki daga Disu Quarters, karamar hukumar Gwale, sai wani mai suna Fatihu Muktar Faruk Kano da kuma Usman Baba Attah, 25, mazaunin unguwar Kabara Quarters, Kano Municipal.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara