DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana zanga-zanga a Kano

-

Zanga-zanga ta barke a Kano duk da haramcin hakan da ‘yan sanda suka yi.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar ta Kano Muhammad Usain Gumel ya haramta wata zanga-zanga da magoya bayan jam’iyyar NNPP da na APC suka bukaci mambobin su da su fito su yi a jihar.
Zanga-zangar dai ta biyo bayan zargin bayar da cin hanci ga sashen shari’a na jihar ya yi ba daidai ba game da batun shari’ar  zaben gwamna na 2023.
Kwamishinan ya ce duk wani yunkurin aiwatar da wannan zanga-zanga, zai zamo wata kafa ta kawo tsaiko ga tsaron kasa.
Sai dai kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, jim kadan bayan fitar da wannan sanarwa, masu zanga-zangar suka yi fitar farin dango, suka cike titunan jihar suka nufi gidan gwamnatin jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara