DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisa na son gwamnati ta yaki cutar ‘malaria’ da karfin tuwo

-

Kwamitin majalisar wakilan Nijeriya kan cutar sida, tarin fuka da cutar zazzabin cizon sauro ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta kafa dokar ta baci kan cutar malari duba da irin hatsarin da ke tattare da cutar.
Shugaban kwamitin Amobi Godwin Ogah ya sanar da hakan a ranar yaki da cutar malari ta duniya.
Ya ce duba da irin hatsarin da cutar ke da shi ya ga ya dace gwamnati ta dauki dukkanin matakan da suka kamata don magance matsalar da yakar sauron da ke haddasa ta.
Amobi Godwin ya bukaci gwamnatoci daga dukkanin matakai da su bullo da tsare-tsaren da za su fatattaki sauro a cikin al’umma.
Dan majalisar ya ce kwamitin zai yi aikinsa ta hanyar bibiyar cibiyoyin kiwon lafiya na yankunan karkara don gani da ido yadda hukumomin kula da lafiya daga tushe ke aiwatar da aikin yaki da cutar zazzabin cizon sauro da alkinta shirin Roll back Malaria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara