DCL Hausa Radio
Kaitsaye

AU ta kori jamhuriyar Nijar daga cikin ta

-

Google search engine

Kungiyar tarayyar Africa ta sanar da korar
jamhuriyar Nijar daga cikin ta, abinda ke zama wani hukunci na baya-bayan nan
da aka yankewa Nijar bayan juyin Mulkin watan jiya.

Bayan taron kungiyar na yau Talata a
birnin Addis Ababa, kungiyar ta ce daukar wannan mataki ya zama wajibi la’akari
da yadda sojojin na Nijar suka ki bada hadin kan da ya dace a game da
tattaunawar Diplomasiyya.

Matakin na AU na zuwa ne bayan da tuni
ECOWAS da wasu kungiyoyin kasashen ketare suka sanar da kakabawa Nijar din
takunkumai, wadanda tuni suka fara tasiri a kanta.

Sai dai kuma masana na ganin
cire Nijar daga cikin AU ba zai yi mata wani tasiri ba, la’akari da yadda kungiyar
ke zama tamkar dai ‘yar amshin shatan kasashen yamma a wasu lokutan.

Bayan wannan
mataki, kungiyar ta AU ta kuma ce zata bibiyi irin matakan da kungiyar ECOWAS
ko CDEAO ta dauka kan jamhuriyar Nijar, don ganin ta inda ya kamata ta kara
shiga da nufin kara matsa lamba ga sojojin na Nijar.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara