DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojojin Najeriya sun ceto karin dalibar Chibok

-

Rundunar sojin Najeriya karkashin Operation Hadin kai sun sanar
da ceto karin dalibar Chibok guda daya.

Google search engine

 

Dalibar na cikin daliban Chibok 276 da ‘yan Boko Haram suka yi
garkuwa da su a ranar 14 ga watan Afrilun 2014 a cikin makarantar su da ke
kauyen Chibok na jihar Borno.

 

Da
yake Karin haske kwamandan rundunar Manjo Janar Gold Chibuisi ya ce bayan likitoci
sun kammala gwaje-gwaje akan dalibar mai suna Mary Nkeki, ya mikata ga hannun
kwamishinan harkokin mata ta jihar Borno Hajiya Zuwaira Gambo. Dalibar mai shekaru
27 ta kubuta daga hannun Boko Haram din ne tare da mijinta wanda shi dan Boko
Haram ne amma ya mika kai ga rundunar sojin mai suna Adamu. 
Bayanai sun nuna cewa sojojin sun yi nasarar gano Mary da
mijinta ne akan iyakar Najeriya da Kamaru a kokarin da suke yi na guduwa daga
sansanin ‚yan Boko Haram din, bayan da mijinta ya kuduri aniyar ajiye makamin
sa. 
Kafofin yada labaran Najeriya sun ruwaito cewa
Mary ta haifi yara guda biyu, sai dai sun mutu a sakamakon matsanaciyar cutar
yunwa da ta kama su lokacin da suke cikin dajin Gulumba dake karamar hukumar
Bama ta jihar Borno.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara