DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsageranci ne a sake gurfanar da ni a gaban kotu-Hudu Ari

-

Google search engine

Dakataccen
kwamishinan zaben jihar Adamawa Barista Hudu Ari ya maka kungiyar lauyoyi ta kasar
a gaban kotu bayan kishin-kishin din da suke yi na  sake gurfanar da shi a gaban kotu.

 

Ari
na wannan barazana ne, bayan da kungiyar ta NBA ta fara
 yunkurin sake gurfanar da shi a gaban kotu kan
zargin yunkurin karkatar da sakamakon zabe, bayan karbar na goro.

A cewar
Ari babu wata hujja da kungiyar ta ke da ita na sake gurfanar da shi a gaban
kotu, kasancewar waccan kotun da aka kai shi ta bada umarnin a tsaya a inda ake
har sai ta kammala binciken da ta ke yi.

Ari ya ci gaba da cewa tsageranci ne ga
kotu idan suka sake gurfanar da shi kan laifi guda, don haka ya bukace su da
kada su kuskura su fara, matukar ba haka ba kuma ta tabbata suma basa mutunta
aiki su.

Tun farko dai ana zargin
Yunusa Ari da ayyana Aisha Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan jihar
Adamawa alhali ba’a ma kammala girka sakamakon zabe ba, dalilin da ya sa aka
rika yada jita-jitar cewa ya karbi cin hancin kudade har naira biliyan guda.

Wannan dalili ne ya
sa hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya ta sanar da dakatar da shi daga
aikin sa sannan kuma aka gurfanar da shi a gaban kotu, sai dai kuma fara shari’ar
ke da wuya kotu ta bukaci a dakata har sai an kammala bincike.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara