DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana karancin naman shanu da na tumaki da dabino a Nijeriya bayan rufe bodar Nijar

-

Safarar shanu, tumaki, dabino da sauran kayan bukata da ake shigowa da su Nijeriya daga Jamhuriyar Nijar ta samu tangarda bayan rufe iyakar kasashen biyu.
Nijeriya dai ta sanar da rufe iyakarta da Nijar bayan da soji suka hambarar da gwamnatin farar hula ta Bazoum a watan 26 gaJuli, 2023.
Wani bincike da jaridar Daily Trust ta wallafa ya nuna cewa kaso mai tsoka na naman shanu da ragunan da ake ci a sassan Nijeriya daban-daban na zuwa ne daga Jamhuriyar Nijar.
Kusan jihohi 6 dai ne suka yi iyaka da Jamhuriyar Nijar da suka hada da Katsina, Jigawa, Yobe, Sokoto, Borno da Kebbi.
‘Yan kasuwa da sauran masu safara na kokawa cewa wannan mataki na gwamnatin Tinubu ya tsayar da harkokinsu cik, inda suka yi roko da gwamnati ta sake duba na tsanaki game da matakin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara