Sojojin da suka yi juyin mulkin Nijar sun bukaci dakarunsu su kasance cikin shirin kare kansu daga hare-haren da suke fargabar za su fuskanta.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce umurnin na kunshe a cikin wata takarda da majalisar koli ta mulkin sojin Nijar ta fitar a ranar Jumma’a. Sai dai kungiyar ECOWAS ta ce ba ta da niyyar afka wa Nijar, illa dai kokari take na mayar da Nijar din tafarkin dimukuradiyy ta hanyar diflomasiyya.