DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji sun yi ikirarin yin sabon juyin mulki a Gabon

-

https://drive.google.com/uc?export=view&id=1g3szG8W_wref_Zv6KR5OQS-4reXtKAj4
Wani gungun manyan jami’an sojin kasar Gaban ya bayyana a kafar yada labaran kasar ta Gabon24, inda ya sanar da karfe iko da hannun gwamnatin Ali Bango.
Kafar yada labaran Aljazeera ta ce sojojin da suka ce sun kifar da gwamnatin ta dimukuradiyya a safiyar Larabar nan sun ce matakin nasu ya biyo bayan mummunan magudin zaben da aka tabka a zaben shugaban kasa na makon da ya gabata da ya bai wa Shugaba Bango karin wa’adin mulki bayan kwashe shekaru 14 a kan karagar mulki.
Sojojin sun ce sun rufe iyakokin kasar tare da rusa shugabancin hukumomin gwamnatin ta Gabon.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara