DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Duk sojan da ba zai yi wa Tinubu biyayya ba, ya ajiye aikin – Janar Takuti

-

Babban Kwamandan rundunar soji ta 81 Manjo Janar Muhammad Takuti Usman ya bukaci jami’an soji a Nijeriya da su ci gaba da yi wa shugaba Bola Tinubu da duk wanda kundin tsarin mulkin kasa ya umurce su biyayya.
Janar Takuti Usman na magana ne a lokacin da ya ziyarci rumbun adana makamai na 35 Artillery Brigade da ke Alamala, Abeokuta jihar Ogun.
Kwamandan sojin ya bukaci sauran sojojin da su kasance masu biyayya tun daga sama har kasa. Kalaman nasa dai na zuwa ne a lokacin juyin mulki ke ta kara fadada a Nahiyar Afrika, a yayin da aka hambarar da gwamnatin Ali Bango na kasar Gabon.
Janar Takuti ya ce rundunar sojin Nijeriya ba za ta lamunci duk wani nau’in rashin da’a ba daga jami’anta ko ma wani daga waje, inda ya ce akwai ‘yan matsaloli nan da can, amma dai ba a wannan sashen adana makamai ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara