DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matashi ya kashe mahaifinsa don yin tsafin da zai kudance

-

Wani matashi mai suna Ridwan dan kimanin shekaru 20 a duniya ya hallaka mahaifinsa domin ya yi tsafin da zai sa ya samu kudi a jihar Ogun.
Kungiyar ‘yan sintirin jihar Ogun dai ne suka yi nasarar kama matashin a yankin Ijebu ta arewa a jihar. Kwamandan sintirin Soji Ganzallo a cikin wata sanarwa ya ce jami’ansa ne suka yi nasara kama matashin a lokacin da suke aikin sintiri, sai suka ji hayaniyar mutane a cikin wani kango.
Ganzallo ya ce da jami’ansa suka kutsa kai cikin gini, sai suka tarar da mutum sharbe cikin jini, wanda ake zargin ya yi aika-aikar ya tsere.
Kwamandan ya ce nan take ya ba jami’ansa umurnin su kamo wanda ake zargin cikin sa’o’i 24, kuma haka aka yi, suka nemo shi a inda ya ke labe a cikin daji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara