DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tura ta kai bango: Dole mu yi yajin aiki – NLC

-

Kungiyar Kwadago a tarayyar Nijeriya NLC ta ce za ta fara wani yajin aikin gargadi na kwanaki biyu daga ranar Talata 5 ga wannan wata na Satumba.
NLC ta ce yajin aikin ya zame mata tilas domin ta nuna adawa da matakin gwamnatin kasar kan nuna gazawarta karara na kasa magance kalubalen da yan kasar ke fuskanta na matsanancin hali sakamakon janye tallafin man fetur ya haifar.
A ranar 2 ga watan Agustan da ya gabata ne dai kungiyoyin kwadago na NLC da TUC suka shirya zanga-zangar lumana a wasu daga cikin manyan biranen kasar domin nuna rashin amincewarsu kan matakin da gwamnatin shugaba Tinubu ta dauka na janye tallafin man fetur.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara