DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mai dokar barci: ‘Yan sanda sun sace babur din ‘yan fashi a Ghana

-

 Jami’an tsaro a birnin
Tamale na arewacin Ghana sun kama wasu ‘yan sanda guda biyu da laifin sace
babur din wasu ‘yuan fashi da aka kama.

Google search engine

Tun farko ‘yan sandan sun
sacewa wasu ‘yan fashi babur din ne bayan da bude wuta a dai-dai lokacin da
wata kotu take gab da yanke hukuncin fashi da makami da ake zargin abokin su da
aikatawa.

Tuni dai aka tsare yan sandan biyu da suka
hadar da Lance Copral Muhammad Aboagye da Sergent Elvis Emmanule, inda kuma aka
bude kundin bincike akan su.

A bincike farko-farko da jami’an tsaro suka
gudanar sun gano cewa dai-dai lokacin da ‘yan sandan ke musayar wuta da mutanen
bayan sun bude wa kotun wuta, a lokacin ne su kuma ‘yan sandan suka zagaya
bayan kotun inda masu laifin suka ajiye ababen hawan su ba tare da wata-wata ba
kuma suka yi awon gaba da mashin din.

Bayan bincike da kama mutanen 13 ne kuma suka
gane mashin din su a lokacin da ake hole su a shalkawatar rundunar ‘yan sandan kasar,
kuma ba tare da bata lokaci ba, suka shaidawa jami’an tsaro cewa wannan shine
mashin din su da aka sace.

Jaridar Ghanian Times ta ruwaito cewa tuni aka
adana mashin din a shalkawatar rundunar ‘yan sandan kasar, yayin da aka fara bincike
don gano sauran Babura 3 da ‘yan fashin suka ce an sace musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara