DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu wanda ya yi barazanar tsige Akpabio daga mukaminsa – Majalisa

-

Majalisar dokokin Nijeriya ta sa kafa ta shure wasu rahotannin da ake yadawa a kafafen watsa labarai cewa wasu fusatattun ‘yan Sanatoci na shirin tsige shugabansu Sanata Godswill Akpabio.
Akwai wasu rahotannin da kafafen yada labarai suka watsa a ranar Asabar cewa ana shirin tsige shugaban majalisar dattawan Nijeriya Sanata Godswill Akpabio.
Rahotonannin sun ce akwai wasu Sanatoci da suka yi wata ganawa ta musamman a kasar Saudi Arabia don su kitsa yadda za a tsige Akpabio.
Sai dai, mai magana da yawun majalisar Yemi Adaramodu a cikin wata sanarwa a ranar Asabar, ya bayyana wadannan rahotannin da cewa ba su da tushe bare makama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara