DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Tinubu za ta mayar da yara milyan 10 makarantun boko

-

Gwamnatin tarayya ta sanar cewa tana nan tana shirin mayar da yara milyan 10 makarantun boko a fadin kasar nan da wasu ‘yan shekaru masu zuwa.
Karamin ministan ilmi Dr Yusuf Tanko Sununu ya sanar da hakan a lokacin da ya karbi bakuncin ‘yan majalisar dokoki na jam’iyyar APC a Abuja.
Babban jami’in kungiyar ‘yan majalisar dokokin wanda shi ne mataimakin shugaban majalisar wakilai Babangida Nguroje bayan taya murna ga ministan, ya bukaci da su saka idanu sosai kan ilmin yara kanana musamman masu karamin karfi.
Sai dai da ya ke mayar da jawabi, Dr Yusuf Sununu ya ce gwamnati na shirin mayar da yara milyan 10 makarantun boko.
Ya ce gwamnati na da burin dasa harsashi mai dorewa a kan ilmi ta hanyar bullo da matakan da za su sa yaran su ji su na son zuwa makarantar ta hanyar samar musu yanayi mai kyau.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara