DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisa ta ja kunnen Tinubu kan kisan kudi ba bisa ka’ida ba

-

Majalisar dokokin Nijeriya ta ja kunnen shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu kan kashe kudi ba bisa ka’ida ba, har ma ta shawarce shi da ya mika mata kasafin kudin cike gibi na ‘supplementary’ musamman kan batun iskar gas.
Majalisar ta hannun shugaban kwamitin majalisa dattawa kan iskar gas Sanata Jarigbe Jarigbe ta bukaci sashen zartarwar da ya mika mata kasafin kudin cike gibi na 2023 don fara aikin inganta bangaren iskar gas.
Wannan bukata dai ta zo ne kasa da sa’o’i 48 bayan da shugaban kasa Bola Tinubu ya sanar da daukar matakan saukaka rayuwa bayan cire tallafin man fetur ga ‘yan Nijeriya.
‘Yan majalisar sun tsaya kai da fata cewa ya kamata a rika kashe kudi a hurumin doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara