DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An rufe kasuwar Mile 12 International Market Lagos

-

Gwamnatin jihar Lagos ta umurci da a gaggauta rufe kasuwannin Mile 12 International Market, da Owode Onirin.
A cikin wata sanarwa daga daraktan hulda da jama’a na ma’aikatar muhalli ta jihar Kunle Adesina ta ce an rufe wadannan kasuwanni ne biyo bayan rashin tsafta da sauran karya dokokin da suka shafi muhalli.
Ya ce an rufe wadannan kasuwanni ne biyo bayan wani aikin hadin guiwa da jami’an LAWMA da na KAI suka gudanar biyo bayan umurnin da suka samu daga kwamishinan ruwa da tsaftar muhalli na jihar Tokumbo Wahab.
Sanarwar ta ce gwamnatin jihar Lagos ba za ta sassauta kan duk wani nau’in tara kazanta ba a ko’ina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara