DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu na cikin jerin musulman duniya 500 da ke da karfin fada a ji

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu na daga cikin jerin sunayen mutane 500 musulmai da ke da karfin fada a ji a duniya.
Kazalika, akwai mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar da mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da karin wadansu ‘yan Nijeriya 12 da ke cikin jerin sunayen mutanen.
Wannan ne karon farko da aka ambato sunan shugaba Tinubu a jerin sunayen musulmai masu karfin fada a ji a duniya da cibiyar kula da harkokin addini ta kasar Jordan ke fitarwa duk shekara.
Sai dai, a wannan sabon bugun, an cire sunan tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari da ya ke yawan fitowa a duk lokacin da aka fitar da sunayen.
Shekh Habib Umar Bn Muhammad Bn Salim Bn Hafiz ne Musulmin da ya fi kowa karfin fada a ji a duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara