DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zubar da mutunci ne dan sanda ya rika karbar N100 daga hannun direbobi

-

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Nijeriya Olumuyiwa Adejobi, ya caccaki jami’an da ke karbar Naira 100 a kan hanya daga hannun masu ababen hawa, inda ya ce jami’an da suke aikata haka suna zubar wa da kansu mutunci ne.
A cewarsa ya kamata ‘yan sandan da ke yin wannan aika-aika su daina saboda suna cin hanci da rashawa.
Adejobi ya bayyana hakan ne a yayin da yake mayar da martani ga wani mai amfani da shafin Tuwita (X) wanda ya tambayi dalilin da ya sa ‘yan sanda ke karbar Naira 100 daga masu amfani da hanyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara