DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mutane milyan 283 na kwana da yunwa a Nahiyar Afrika – Adesina

-

Shugaban bankin bunkasa Nahiyar Afrika Dr Akinwumi Adesina ya sanar cewa mutane milyan 283 na kwana da yunwa a Nahiyar Afrika.
Dr Adesina na magana ne a taron daidaita farashi a kasar Amurka, inda ya ce bankin ya ware wasu kudi Dala bilyan 1 don tallafar jihohi 24 na Nijeriya.
Ya ce hakan wani kari ne daga Dala Milyan 520 da aka tura don inganta aikin gona da zummar abinci ya wadata.
Shugaban bankin ya ce an yanke shawarar kai wannan dauki a Nijeriya don a bunkasa sassan aikin gona saboda yawan kasar noma da Allah Ya huwace mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara