DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matsin rayuwa ya sa ana samun mutanen da ke kwana 3-4 ba su ci abinci ba – Mustapha Inuwa

-

Tsohon Sakataren Gwamnatin jihar Katsina Mustapha Muhammad Inuwa ya ce yanzu ana wani yanayi na matsin rayuwa da har ta kai mata na cewa mazajensu sun rasu don a taimake su alhali mazan na nan da ransu.
Mustapha a wata zantawa da ya yi wasu kafafen yada labarai na zamani a Katsina, ya ce yanzu haka ana samun mutanen da ke kwana 3-4 ba su ci abinci ba, hasalima, ba su kirguwa a cikin al’umma a wannan yanayin da ake ciki.
Mustapha Inuwa wanda ya yi wa APC takarar Gwamna a jihar Katsina a zaben 2023, ya koka kan irin halin karancin tsaro da sassan jihar ke fama da shi, inda ya yi addu’ar duk masu amfana da yanayin matsalar tsaro da ake ciki, “muna addu’ar Allah Ya yi mana maganinsu”.
Ya koka cewa idan aka ci gaba da tafiya haka a kasar nan, ba a san halin da ‘ya’ya da jikoki za su shiga ba a rayuwarsu ta gaba.
Mustapha Muhammad Inuwa ya ce “Ni dan siyasa ne, ba dan takara ba. Tun daga lokacin da aka kammala zabe, har ya zuwa yanzu, ban taba tafiyar da na kwana bakwai bani Katsina ba. Kuma ina iya wata biyu cur, ban bar Katsina ba. Gidana a bude yake ga kowa, haka ofis dina, duk rana sai na je”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara