DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Na fi Akpabio kwarewa da gogewa a aikin majalisa – Ndume

-

Sanata Ali Ndume mai tsawatarwa na majalisar dattawan Nijeriya, ya sanar cewa ya fi shugaban majalisar Sanata Godswill Akpabio gogewa da kwarewa a aikin majalisa.
Sanata Ndume da ke wakiltar Borno ta Kudu ya sanar da hakan ne a cikin wani shirin gidan talabijin na Channels, Abuja.
Tun dai a shekarar 2011, Sanata Ali Ndume ya ke majalisar dattawan, amma shi Akpabio ya fara zuwa majalisar dattawan ne a shekarar 2015.
Sanata Ndume dai ya sanar da dalilinsa na ficewa daga majalisar a lokacin da Akpabio ya katse shi lokacin da ya ke magana a majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara