DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar Zamfara ne a gabana – Gwamna Dauda

-

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawan Dare ya ce har yanzu bai yi kasa a guiwa ba wajen tabbatar da rantsuwar da ya sha ta kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar Zamfara.
Dauda Lawan Dare na magana ne a Masarautar Maru ta jihar da ya je ziyarar ta’aziyya da jajantawa bisa hare-haren ta’addanci da suke fama da su.
Gwamnan ya yi ta’aziyya ga Masarautar da daukacin al’ummar wannan masarauta bisa ayyukan ta’addanci da ke wakana ga al’ummar yankin.
A yayin ziyarar, Gwamnan tare da Mai Martaba Sarkin Maru Alhaji Abubakar Gado sun gudanar da sallar Juma’a a babban masallacin garin, inda aka gabatar da addu’o’i na samun zaman lafiya a yankin da ma jihar bakidaya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara