DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga na tursasa wa manoma su biya haraji kafin su girbe amfanin gonakinsu a Kaduna

-

‘Yan bindiga na tursasa wa wasu manoma a wasu kauyukan jihar Kaduna su biya haraji kafin su kyale su, su girbe amfanin gonakinsu da suka noma a daminar bana.
Kauyukan da lamarin ya shafa sun hada da na Kidandan da Galadima a karamar hukumar Giwa, sai mutanen kauyen Angular Fala’u da na Kerawa suka ce kodayaushe ‘yan ta’addar na yin garkuwa da su a duk lokacin da suka je girbin amfanin gonakinsu.
Wani mazaunin kauyen Kidandan Malam Jamil, ya ce al’ummar kauyensu na biyan kudin harajin da suka kai Naira 70,000 zuwa 100,000 don su girbe amfanin gonakinsu.
Ya ce wadanda suka ki ko gaza biya, za a sace su ko a kashe ko kuma ‘yan bindigar su kwace amfanin gonakin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara