DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya gaza wajen yaki da cin zarafin dan adam-Amnesty International

-

Google search engine

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International
ta zargi shuga Tinubu da kau da idanu game da yadda ake amfani da karfi wajen
cin zarafin jama’a a Najeriya.

 

A wata makala da
kungiyar ta fitar mai taken tsarin yaki da cin zarafi a Najeriya, ta ce cikin watanni
shidan da Tinubu ya yi a Office bai tsinana komai ba, game da yaki da cin
zarafin jama’a.

Makalar da kungiyar
ta gabatar a Abuja, ta kunshi misalai game da yadda aka ci zarafin jama’a amma
gwamnati ta yi shiru.

Amnesty
International ta kuma ce abin takaici ne yadda kundin sabbin tsare-tsare da
gwamnati ta bijiro da su basu kunshi irin yadda za’a yaki cin zarafin jama’a
ba.

Sai dai kuma kungiyar ta ce har yanzu lokaci bai kurewa Tinubu
ba, don kuwa yana da damar da zai kawo karshen wannan matsala.

Shawara ta farko da hukumar ta baiwa Shugaba Tinubu shine ya yi kokari
wajen tabbatar da ganin an hukunta masu aikata wannan laifi.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara