DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An gano inda ake hada-hadar cinikin kodar bil’adama a Abuja

-

Wani zurfaffen bincike da jaridar Daily Trust ta gudanar ya gano inda ake sayar da kodar bil’adama a babban birnin tarayya Abuja.
Binciken ya gano cewa a kasuwar ta bayan fage, ana sayar da duk koda daya kan kudi Naira milyan daya.
Kazalika, an gano yadda ake yaudarar mutane musamman masu karamin karfi ta yadda za a ja ra’ayinsu, su sayar da kodar su.
An dai gano cewa wannan sana’a ta jima ana gudanar da ita, musamman a yankin Mararaba da ke kusa da birnin tarayya, amma garin ya ke a karamar hukumar Karu ta jihar Nasarawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara