DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsadar rayuwa ta sa ‘yan Nijeriya na jin haushin jami’an gwamnati – Kasshim Shettima

-

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya ce yanzu haka ‘yan Nijeriya na jin haushin jami’an gwamnati da sauran ‘yan boko ganin irin halin matsin rayuwa da hauhawar farashi ta haddasa a kasar.
Mataimakin shugaban kasar na magana ne a Abuja a wajen taron da cibiyar nazarin tsaro ta shirya.
Jaridar Punch dai ta rawaito cewa wannan ne karon farko da aka ji wani jami’in gwamnati ya amsa cewa ana cikin yanayi na matsin rayuwa a Nijeriya tun bayan da Bola Tinubu ya karbi ragamar tafiyar da kasar a Mayun 2023.
Kasshim Shettima ya ce akwai ‘yan Nijeriya masu karamin karfi da ke jin haushin wadanda suke ganin sun samu rufin asiri. Har ya buga misali da cewa a Maiduguri, idan mutum ya sayo sabuwar mota, mutane na mayar da gidansa kamar wani wajen neman gafara ta yadda mutane ke yawan zuwa ziyara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara