DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a kashe Naira milyan 173 don samar da lantarki ta hasken rana a asibitin Dutse, jihar Jigawa

-

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da a fitar da kudi Naira milyan 173 don aikin samar da lantarki ta hasken rana a babban asibitin da ke Dutse, babban birnin jihar.
Kwamishinan yada labaran jihar Sagir Musa ya sanar da hakan ga manema labarai, inda ya ce majalisar zartarwar jihar ce ta amince da hakan bayan taron da ta gudanar a ranar Alhamis.
Kwamishinan ya ce wannan matakin ya biyo bayan kudirin Gwamnan jihar Umaru Namadi na kyautata babban asibitin jihar don samar da kiwon lafiya mai inganci ga al’ummar jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara