DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An damfari ‘yan Nijeriya sama da 1,000 da sunan za a ba su aiki a Ingila – IOM

-

Hukumar da ke kula da masu gudun hijira ta majalisar dinkin duniya IOM ta ce akwai ‘yan Nijeriya sama da dubu daya da aka damfara da sunan za a samar musu aiki a kasar Ingila.
Babban jami’in hukumar a Nijeriya Laurent De Boeck ya sanar da hakan a Abuja a lokacin da yake ganawa da manema labarai.
Mr Boeck ya ce kusan kowanensu ya yi asarar kudin da suka kai darajar Dala dubu 10,000 ta dalilin neman aikin, amma ba a yi kwado da yaro ba kuma ba a bashi gayansa ba.
Mr Laurent ya ce idan suka je ma’aikatun suka gabatar da takardun kama aikin da aka damfare su aka ba su, sai ma’aikatun su ce wannan takarda ba daga gare su take ba.
Ya ce da yawansu suna can sun yi tsuru-tsuru a Ingila ba su da kudin komowa Nijeriya, a yayin da wasu kuma ke kunyar dawowa su tunkari iyalansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Yadda ‘yan cabals ke turawa Buhari takardu a boye don ya sanya musu hannu – Tsohon shugaban ma’aikata, Gambari

Tsohon shugaban ma’aikata na Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana yadda wasu makusantan shugaban suka rika tsallake shi tare da mika takardu...

Mafi Shahara