DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisa sun kori kwamishinan kasafin kudin daga zauren majalisar dokokin jihar Zamfara

-

‘Yan majalisar dokokin jihar Zamfara sun bukaci da kwamishinan kudi na jihar Abdulmalik Gajam da ya fita daga zauren majalisar a lokacin da Gwamna Dauda ya gabatar musu da daftarin kasafin kudin 2024.
‘Yan majalisar dai sun ce sun dauki wannan matakin ne biyo bayan kin mutunta gayyatar majalisar da suka ce kwamishinan ya yi, na ya je gabansu don kare kasafin kudin shekarar 2024.
Bayan tattaunawa, majalisar ta amince cewa takardar tabbatarwar da ta ba kwamishinan tun da farko, ta janye.
Kamar yadda suka ce, sun gayyaci kwamishinan sau uku don ya je majalisar ya kare kasafin kudin shekarar 2024 na ma’aikatarsa, amma ya ki zuwa, kuma bai bayar da wata hujja mai kwari ba.
Bayan kammala bayyana wadannan dalilai na su, ‘yan majalisar sun bukaci kwamishinan da ya fita daga zauren majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara