DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An kai kudirin neman majalisa ta amince ‘yan Nijeriya su rika kare kansu daga ta’addanci

-

Majalisa

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna kan kudirin da zai ba ‘yan kasa damar mallakar makamai domin kare kansu.

Jaridar Leadership ta ruwaito sanata mai wakiltar Delta ta Arewa a majalisar Prince Ned Nwoko ne ya gabatar da kudirin dokar, domin yin gyara a dokar da ake da ita ta mallakar makami ga farar hula.

Google search engine

Ya kara da cewa barazanar tsaro da ‘yan kasa ke fuskanta ya sa mutane da yawa cikin halin kunci da rashin kwanciyar hankali inda ya kara da cewa kudirin nasa zai baiwa fararen hula damar mallakar makamai da za su kare kansu.

Daga karshe Sanatan ya yi fatar abokan aikin nasa za su goyi bayan kudirin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara