DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hisbah na fatar takaita barace-barace a Katsina

-

Hukumar Hisba a jihar Katsina ta ja kunnen iyaye akan su kula da yaransu, kuma su ja kunnensu kafin su fara kai samame a gidajen baɗala a jihar.

Kwamandan hukumar Sheikh Aminu Usman Abu-Ammar ne ya faɗi hakan a cikin wani faifan bidiyo yana mai cewa duk mahaifin da ya san ɗansa yana tattara daba a cikin unguwanni, to su kuka da kansu.

Google search engine

Abu-ammar ya ce duk ɗan da ya kuskura ko mahaifin da ya sake ya shigo hannun hukumar zai fuskanci fushin hukuma.

“Zamu shiga lungu da sako domin mu tsawatar, ayi dai-dai”

“Aikin hukumar Hisba ne umarnin da kyakkyawa da kuma hani da mummuna, wannan shi ne jigon aikin hukumar’

Ya kara da cewa “Manufar hukumar shi ne a taimake ka ɗan ka ya zama ingantacce, saboda nauyi ne na hukuma ta yi aikin da za ta inganta al’ummar da take jagoranta.”

Kwamandan ya kara da cewa hukumar za ta yi kokari wajen taƙaita barace-batace a bisa titunan jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Yadda ‘yan cabals ke turawa Buhari takardu a boye don ya sanya musu hannu – Tsohon shugaban ma’aikata, Gambari

Tsohon shugaban ma’aikata na Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana yadda wasu makusantan shugaban suka rika tsallake shi tare da mika takardu...

Mafi Shahara