DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan tsaro Matawalle ya gabatar da jiragen ruwa marasa matuki ga Tinubu

-

 

Google search engine

Ministan kasa a Ma’ikatar Tsaron Nijeriya Mohammed Bello Matawalle, ya gabatar ma Shugaban kasa Bola Tinubu jiragen ruwa marasa matuki guda biyu a fadar shugaban kasar da ke Abuja.

Hakan na kunshe a wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai Henshaw Ogubike ya fitar a Abuja.

Sanarwar ta ce Ministan ya shaida wa shugaban kasa cewa, Jiragen biyu za su taimaka wajen yaki da ta’addanci a bakin gabar ruwa.

Matawalle ya sanar da Tinubu cewa wadannan jirage na da nufin inganta sabbin fasahohin da za su kara wa sojojin Najeriya kwarin gwiwa wajen tunkarar kalubalen tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara