DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NDLEA ta kama matar da ke kai wa ‘yan ta’adda makamai a Katsina

-

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya NDLEA ta sanar da kama wata mata mai suna Bilkisu Sulaiman da ake zargi da safarar makamai ga ‘yan ta’adda a jihar Katsina.
Kamar yadda sanarwar da ta fito daga kakakin hukumar na kasa Femi Baba Femi, ta ce an kama matar mai shekaru 28 na safarar makaman ne kan titin Zaria-Kano, inda take burin kai makaman a kauyen Kakumi na karamar hukumar Bakori ta jihar Katsina.
Hukumar ta ce an samu matar da harsasai 249 da aka kulle a cikin bakar leda aka saka cikin karamar jikkar hannu.
Femi ya ce bayan kama matar, an kai ta Ofishin ‘yan sanda na jihar Kaduna don karasa bincike a kanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara