DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu za ta yanke hukunci kan shari’ar Barr Muhyi a ranar Juma’a

-

Kotun kula da ma’aikata ta CCB da ke zamanta a Abuja, ta sanar da ranar Juma’a 12 ga watan Janairu, 2024 a matsayin ranar da za ta yanke hukunci kan shari’ar Barr Muhyi Magaji Rimin Gado.
Muhyi Rimin Gado dai shi ne shugaban hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci ta jihar Kano PCACC.
Kotun dai ta ba da wannan matsayar ne a Larabar nan bayan zaman da ta gudanar karkashin jagorancin Mai Shari’a Danladi Umar.
Kamfanin Dillancin labaran Nijeriya NAN ya ba da labarin cewa a ranar 16 ga watan Nuwambar 2023, kotun ta tsare Muhyi Magaji Rimin Gado, inda take tuhumarsa da laifuka 10.
Sai dai Barr Muhyi ya kiya amsa laifin, har ma ya nemi a ba da shi beli, karshe kotun ta ba da shi beli kan kudi Naira milyan 5 da masu tsaya masa guda biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara