DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wani fasinja ya gartsawa ma’aikaciyar Jirgi cizo.

-

 Fasinja ya gartsa wa ma’aikaciyar jirgin sama cizo

Google search engine

Wani jirgin sama a kasar  Japan da ke kan hanyarsa ta  zuwa Amurka ya koma birnin Tokyo bayan da wani fasinja da ya bugu da giya ya ciji wata mata ma’aikaciyar jirgin da hakan ya tilasta wa matukin jirgin saukar gaggawa.

An ruwaito cewa mutumin mai shekaru 55 da ake kyautata zaton Ba’amurke ne, ya ciji matar a  hannunta, inda har ya ji mata  rauni, kamar yadda mai magana da yawun kamfanin All Nippon Airways ya shaida wa kamfanin dillacin labarai na AFP.

Lamarin da ya sa matukan jirgin da fasinjoji 159 suka  zuwa filin jirgin Haneda, inda aka mika mutumin ga ‘yan sanda. 

Kafar yada labarai ta kasar Japan TBS ta ruwaito fasinjan yana fadawa masu binciken cewa “bai san ya aikata laifin ba”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara