DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a kashe N32bn don kwaskwarima ga ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro

-

Kimanin watanni 8 kenan da gina katafaren ginin da a yanzu haka hukumar kula da harkokin tsaro ta kasa ta ware Naira biliyan 31.915 a cikin kasafin kudin shekarar 2024 domin yin sabbin gine-gine.

Google search engine

Wannan dai ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun yawaitar kashe-kashe da sace-sacen al’umma a wasu jihohin Nijeriya, ciki har da babban birnin tarayya Abuja, inda ‘yan bindiga ke sace jama’a daga gidajen su da wuraren kasuwancinsu.

A ranar 21 ga Maris, 2023, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya kaddamar da katafaren ginin ofishin harkokin tsaron na kasa da Cibiyar Yaki da Ta’addanci ta Kasa (NCTC), wadanda suka lakume biliyoyin Nairori.

A lokacin da yake kaddamar da wasu cibiyoyi guda biyu na zamani a Abuja, ya ce an yi su ne don inganta da magance matsalolin tsaro a kasar nan, musamman ta’addanci ayyukan bata gari.

Sabbin gine-ginen suna dauke da manya-manyan ofisoshi tareda babban dakin taro da cibiyoyin nazari da bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara