DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan siyasa ne ke dagula harkokin zabe a Nijeriya – Ganduje

-

Shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje ya yi kukan cewa da yawa daga cikin ‘yan siyasar kasar ne ke dagula lamurran zabukan da ake gudanarwa.
Ganduje na magana ne a lokacin da ya karbi bakuncin daraktar sa ido kan harkokin zabe da jam’iyyun siyasa Hawa Habibu, inda ya ce yana sane cewa babbar matsalar gudanar da zabe a Nijeriya ita ce batun tsaro, amma ba haka bane, ‘yan siyasa ne babbar matsalar.
Ya ce akwai bukatar hukumar zabe INEC ta bullo da tsarin fadakar da jama’a kan illolin yin karan-tsaye ga harkokin zabe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara