DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar Dattawa zata gayyaci Wike kan matsalar tsaro a abuja.

-

 Majalisar dattawa za ta gayyaci Wike kan matsalar satar mutane a abuja. 

Google search engine

Sanata mai wakiltar babban birnin tarayya abuja, Ireti Kingibe, ya ce majalisar dattawa za ta gayyaci ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, kan karuwar rashin tsaro da ayyukan ta’addanci a Abuja.

Kingibe, ya bayyana hakanne yayin zantawarsa da manema labarai a jiya Lahadi inda ya bayyana cewa Majalisar Dattawa za ta gayyaci Wike da shugabannin hukumomin tsaro kan yawaitar laifuka a abuja.

Yace, Lokacin da Majalisar Dattawa ta dawo aiki, an shirya cewa kwamitin (Majalisar Dattawa) na bukatar ya zauna da ministocin biyu da hukumomin tsaro domin su basu tsare-tsarensu na tsaro domin Kawo Karshen matsalar tsaron a abujar. 

wannan shi ne tsarin da ake gani zai kare al’ummar babban birnin tarayyar abuja. domin da ministan abuja, Kwamishinan yansanda da shugaban DSS, Yakamata suyi tsari maikyau wajen kawarda  Matsalar tsaro a yankin. 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara