DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Raɗɗa ya umarci jami’an gwamnatinsa su ayyana kadarorin da suka mallaka

-

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, ya bayar da tabbacin cewa duk masu rike da mukaman siyasa da na gwamnati a jihar za su bayyana kadarorin su.

Google search engine

Raɗɗa ya bayar da wannan tabbacin ne a jiya Litinin a lokacin da ya karbi baƙuncin shugaban hukumar da’ar ma’aikata, Barista Murtala Aliyu Kankia, a fadar gwamnatin jihar.

A jawabin nasa shugaban hukumar da’ar ma’aikata, Barr. Aliyu Kankia ya bayyana irin rawar da Ofishin sa ke takawa, ba wai kawai sa ido kan bayanan kadarori ba, har ma da tabbatar da bin ka’idojin na da’a ga jami’an gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara