DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yadda wani dan sanda ya ki karbar tayin cin hancin naira miliyan 1 daga hannun mai garkuwa da mutane

-

Wani dan sanda da ke aiki karkashin rundunar yan sanda ta jihar Kaduna ya
ki karbar cin hancin Naira miliyan 1 da wani kwararren mai garkuwa da mutane ya
bashi.

Google search engine

 

Bayanai sun ce yan sanda sun yiwa dan
garkuwa da mutanen kofar rago ne a wani Otal mai suna Tafa, kuma nan take yayi wa
dan sandan tayin naira miliyan 1 cikin kudin fansar da ya karba, sai dai dan
sandan ya ki karba.

Ko da yake jawabi mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ASP Mansir
Hassan ya ce sun sami bayanan sirri ranar 19 ga watan da muke ciki na Agusta
cewa dan garkuwa da mutanen ya sauka a wannan Otal din nan take kuma suka aike
da jami’an su inda suka kama shi.

ASP Mansir ya ce an yi nasarar kwato sama
da naira miliyan 2 da dubu 350 a hannun mai garkuwa da mutanen da aka bayyana
sunan sa da Bello Muhammad mai shekaru 28 dan asalin jihar Zamfara.

Rahoton binciken farko-farko na yan sanda
ya nuna yadda dan bindigar ya shaida musu cewa yana cikin ‘yan ta’adda da ke
addabar yankin dajin Kagarko na jihar Kaduna.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara