DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba haka ake zawarcin shiga jam’iyya ba, Gwamna Abba ya yi wa Ganduje martani

-

 Ba haka ake zawarcin shiga jam’iyya ba, Gwamna Abba ya yi wa Ganduje martani

Google search engine

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf  ya ce ba shi da niyyar ficewa daga jam’iyyar sa ta (NNPP) da ya ci zabe a karkashinta. 

Gwamna Abba ya bayyana hakan ne kwana daya bayan da shugaban jam’iyyar APC Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bashi goron gayyatar komawa jam’iyyar APC.

Gwamna Abba Kabir, wanda kotun koli ta tabbatar da shi a matsayin Gwamnan jihar Kano a ranar Juma’a 12 ga watan Janairu shi ne kadai gwamna a jam’iyyar NNPP a Nijeriya.

A yayin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da ya gudana a  Kano, Ganduje ya yi kira ga Gwamna Abba Kabir tare da mambobinsa da magoya bayansa na jam’iyyar NNPP da su sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki a matakin kasa domin tabbatar da ci gaban siyasar jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara