DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba mu karbi takarda a hukumance daga kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso ba – ECOWAS

-

Kungiyar kasashe masu tattalin arziki ta ECOWAS ta ce har yanzu ba ta karbi wata sanarwa ko takarda a hukumance da ke nuna sun fice daga cikin kungiyar.
A cikin wata sanarwa daga sakatariyar kungiyar ta ce kawai abin da ta sani shi ne tana aiki ba gajiyawa wajen maido da kasashen bisa turbar dimokradiyya.
Ta sanar cewa har yanzu kasashen na da matukar amfani a tafiyar da lamurran kungiyar.
A ranar Lahadin nan dai, kasashen uku na Mali, Nijar da Burkina Faso suka sanar cewa sun fice daga kungiyar ta ECOWAS inda suka ce ana musu barazana. Kasashen uku dai na karkashin jagorancin sojoji bayan da suka hambarar da gwamnatin farar hula.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara