DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun yaba wa NAHCON da ta nemo ragin kudin kujerar aikin hajji ga ‘yan Nijeriya – IHR

-

Kungiyar masu aike wa da rahotannin yadda aikin hajji ke gudana ta ‘Independent Hajj Reporters – IHR’ ta yi jinjina ga hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON da ta nemo wa maniyyata aikin hajjin bana na kasar sauki wajen farashin kujerar zuwa aikin hajji a shekarar 2024.
A cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar mai zaman kanta Alhaji Ibrahim Muhammad, ta ce tana sane cewa kudin aikin hajjin bana na iya kaiwa Dala 6,000 kwatankwacin Naira milyan 8,400,000 a kudin Nijeriya idan aka sayar da Dala daya kan kudi N1,400.
Sai kungiyar ta ce bayan yunkurin da hukumar NAHCON ta yi, yanzu duk a fadin Nijeriya, karshen kudin zuwa aikin hajjin shi ne Naira milyan 4.9 da zai taimaki ‘yan Nijeriya su samu rarar kudin da suka kai kusan Naira milyan biyu ga yadda Saudiyya ta tsara za a biya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Yadda ‘yan cabals ke turawa Buhari takardu a boye don ya sanya musu hannu – Tsohon shugaban ma’aikata, Gambari

Tsohon shugaban ma’aikata na Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana yadda wasu makusantan shugaban suka rika tsallake shi tare da mika takardu...

Mafi Shahara