DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kebbi ta rufe wasu kwalejojin kiwon lafiya guda biyu

-

Gwamnatin jahar Kebbi ta rufe wasu man’yan makarantu biyu masu zaman kansu bisa rashin biyan haraji har na tsawon shekaru biyu.

Google search engine

A wata sanarwa da ta fito daga ofishin Kwamishinan ilimin na jahar Isa Abubakar Tunga ta nuna cewa gwamnati bazata yi musu da wasa ba saboda sakaci da suka yi bayan tunatar da su da kuma kashedi da gwamnati ta yi garesu a lokuta daban-daban.

Makarantun da aka rufe sune Kwalejin ilimi da kimiyyar kiwon lafiya ta LamiÉ—o Umaru Mutube da ke ĆŠakin- Gari da Kwalejin Kimiyya da fasahar kiwon lafiya ta SAHAM da ke Zuru.

Gwamnatin ta Kebbi ta ce babu wata bita da Ć™ulli a batun dakatarwa kuma da zĂŁrar sun biya kuÉ—aÉ—en da gwamnati ke bin su za’a buÉ—e makarantun su ci gaba da harkokin karantarwa.

Binciken hukumar kula da ilimi ta Majalisar Ɗinkin Duniya UNESCO na 2012 ya nuna cewa Jihar Kebbi dai na daga cikin jihohin Najeriya da ke baya a ɓangaren ilimi bayan jihohin Katsina, Taraba, Borno da Jigawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara