DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar APC ta yi gargadi kan rusa masarautun Kano

-

 Jam’iyyar APC ta yi gargadi kan rusa masarautun Kano. 

Google search engine

Jam’iyyar adawa ta APC ta gargadi gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da ya yi taka-tsan-tsan don gudun kada a tura shi yin wani abu da zai iya shafar zaman lafiya da ake samu a jihar Kano. 

 Jam’iyyar APC ta yi gargadin cewa duk wani yunkuri na kawo cikas ga tsarin masarautun, kamar yadda Ganduje ya kirkiro, na iya tayar da zaune tsaye a garin muddin suka dauki matakin hakan kamar yadda jaridar Punch ta rawaito.

A ranar 5 ga watan Fabrairu ne wata kungiya mai suna‘Yan Dangwalen Jihar Kano ta rubutawa Majalisar Dokokin Jihar Kano, takardar neman a sake duba dokar kafa karin masarautu hudu a Gaya, Rano, Karaye, da Bichi da gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje ta yi.

Kungiyar ta kuma yi kira da a mayar da tsohon Sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara